Categories
Labaran Duniya Nishadi Rahoto Siyasa Wasanni

Mutane 15 doka tasa halewa ayi musu jiniya a Najeriya -Abba Hikima

Duk Nigeria mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya. A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa. Kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata sahalewa ba zaman gidan yari ne na wata 6.

Barin mutanen da basu cancanci a musu jiniya ba yin amfani da ita yana kara kumbura musu kai. Yana sa su girman kai da raina mutane. Kuma ya jawo raina doka.

Saboda haka, ya kamata yan sanda su kama wannan mata su gurfanar da ita a gaban kotu a bisa wannan laifi da sauran laifuffukan da suka fito fili.

Kuma indai shugabanni; zababbu da nadaddu basu takawa matan su da iyalan su birki akan shiga harkokin mulki ko bawa jami’an Nigeria umarni ba, to zaune bata kare mana ba a wannan kasa. Dan na tabbata wata rana wata shafaffiya-da-man in taci ta koshi, cewa za tayi a kamo mata shugaban sojoji.

Categories
Nishadi

Na taɓa samu kyautar Naira miliyan Arba’in-(40m)

An taba bani kyautar kudi N40m inji wata ‘yar fim

Tauraruwar fina-finan kudancin Nijeriya Nollywood Toyin Abraham ta ce tana matukar kaunar bayyana a Talabijin domin nishadantar da mutane ba wai don ta samu kudi ba.

Tauraruwar da ta bayyana a cikin shirin ‘Rubbin Minds’ na gidan Talabijin na Channels, ta ce a harkar fim ta samu kudi ta yi arziki a saukake.

‘Yar kimanin shekaru 40, Toyin Abraham ta ce ta fara samun kudi a harkar fim shekaru 5 da suka gabata. Ta ce bata mantawa lokacin da aka kira ta a waya don ta tura lambar bankin ta.

Bayan tura lambar bankin ne ta ga kamar a mafarki, an tura mata kudi jibge har Naira milyan 40, inda ta ce hakan sai da ya sa bacci ya gagare ta.

Design a site like this with WordPress.com
Get started