Categories
Siyasa

‘Yan sandan Kano sun hada kai da gwamnati domin cutar da mu – NNPP

Rabi’u Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar NNPP

Rabi'u Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa karkashin jam'iyyar NNPP

Jam’iyyar NNPP a jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta zargi kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mamman Dauda da hada kai da gwamnatin jihar ta APC domin kawo mata nakasu a zabe mai zuwa.

A wani taron manema labarai da ta kira, Jam’iyyar ta NNPP ta ce kwamishinan ‘yan sandan ya kame mambobinta sama da 100 ba tare da wani dalili ba, inda ta yi kira ga babban sufeton ‘yan sandan kasar ya cire kwamishinan jihar.

Dr Abdullahi Baffa Bichi, wanda shi ne dan takarar Sanata na jam’iyyar, ya shaida wa manema labaran cewar sun bada tsawo sa’o’i 24 a saki mambobinsu ko su tsunduma zanga-zangar lumana.

Wakilin RFI Hausa, Abubakar Abdulkadir Dangambo ya yi kokarin jin ta bakin ‘yan sandan na Kano kan wannan zargi, sai dai har zuwa yanzu kakakin rundunar bai amsa kiran da manema labarai suka yi masa ba.

Kazalika, ita ma gwamnatin Kano ba ta ce komai tukunna game da zargin.

Categories
Siyasa

A rana mai kamar irin ta yau ne a kashe tsohon shugaban Najeriya-Murtala Ramat

A rana mai Kamar Ta Yau 13 ga Fabrairun 1976, A ka kashe Shugaba mulkin Soja Na Tarayya Najeriya General Murtala Ramat Muhammad a Wani yunkurin juyin mulki.

An kuma kashe direbansa Da Gwamnan Mulkin Soja Na jihar kwara Kanal Ibrahim Taiwo.

Yunkurin juyin mulkin Nijeriya a shekarar 1976 wani yunkuri ne na juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijeriya ranar 13 ga Fabrairun 1976 a lokacin da wani bangare na hafsoshin Sojin kasar karkashin jagorancin Laftanar Kanar Bukar Suwa Dimka suka yi yunkurin kifar da gwamnatin Janar Murtala Mohammad. (wanda ya karbi mulki a juyin mulkin 1975 ).

An kashe Janar Murtala Muhammad a Legas tare da mataimakinsa Laftanar Akintunde Akinsehinwa a lokacin da wasu sojoji karkashin Dimka suka yi wa motarsa ​​kwanton bauna a Ikoyi kan hanyar zuwa Barrack Dodan. A cikin shirye-shiryen Rediyo Da Aka watsa ga al’ummar kasar, Dimka ya ambaci cin hanci da rashawa, yanke hukunci, kamawa da tsarewa ba tare da shari’a ba, Da rauni daga bangaren Gwamnatin Murtala da rashin iya gudanar da mulki a matsayin dalilan kifar da gwamnati.

Sojojin gwamnati Masu Biyayya Ga Gwamnati sun murkushe yunkurin juyin mulkin bayan sa’o’i da dama.

Bayan farautar makwanni uku, Ana Neman Dimka Daga Bisani an kama Dimka a kusa da Abakaliki a kudu maso gabashin Najeriya a ranar 6 ga Maris 1976.

Laftanar Janar Olusegun Obasanjo ne ya gaji Janar Murtala Muhammad a matsayin shugaban kasa.

A lokacin da mulkin Obasanjo tare da makaranban shi a Gwamnati, da suka hada da  shehu Musa Yar’adua da TY Danjuma da IBB da Domkat Bali sun yi kokarin ganin sun aiwatar da ayyukuna da Murtala ya kudurta gudanarwa a Najeriya.

Saboda kimar Janar Murtala Muhammad ne a Najeriya, aka saka hotonsa cikin kakin Soji a kudin kasar Naira Ashirin.

Categories
Siyasa

Shugaba Buhari na shirin tafiya a kasar Senegal

Buhari

Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari zai tafi ƙasar Senegal ranar Talata domin halartar taron ƙasa da ƙasa kan harkokin noma karo na biyu da za a gudanar a birnin Dakar.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Femi Adesina ya fitar ranar Litinin.

Taron wanda shugaban Senegal kuma shugaban ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU, Macky Salla zai karɓi baƙunci – an shirya shi ne domin samar da kyakkyawan yanayin noma domin ciyar da haniyar Afirka.

Mista Adesina ya ce maharta taron za su tattauna batun shigar da abinci da sauran kayan amfanin gona zuwa wasu ƙasashen, ciki har da Najeriya.

Ya ƙara da cewa yayin da nahiyar Afirka ke da mutum miliyan 249 da ke cikin ƙagin yunwa, taron – wanda shugabannin ƙasashen Afirka da ministocin kuɗaɗen da na noma na nahiyar, da ƙungiyoyin duniya za su halarta – zai saka aniyar kawar da yunwa a nahiyar Afirka nan da shekarar 2030.

Daga cikin tawagar da za ta yi wa shugaba Buhari rakiya zuwa taron har da ministan harkokin ƙasashen waje, Geoffrey Onyeama, da ministan noma da raya karkara, Dakta Mohammad Mahmood Abubakar, da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Babagana Monguno da daraktan hukumar tattara bayanan sirri ta ƙasar Ambassada Ahmed Rufai Abubakar.

Article share tools

Categories
Labaran Duniya Nishadi Rahoto Siyasa Wasanni

Mutane 15 doka tasa halewa ayi musu jiniya a Najeriya -Abba Hikima

Duk Nigeria mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya. A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa. Kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata sahalewa ba zaman gidan yari ne na wata 6.

Barin mutanen da basu cancanci a musu jiniya ba yin amfani da ita yana kara kumbura musu kai. Yana sa su girman kai da raina mutane. Kuma ya jawo raina doka.

Saboda haka, ya kamata yan sanda su kama wannan mata su gurfanar da ita a gaban kotu a bisa wannan laifi da sauran laifuffukan da suka fito fili.

Kuma indai shugabanni; zababbu da nadaddu basu takawa matan su da iyalan su birki akan shiga harkokin mulki ko bawa jami’an Nigeria umarni ba, to zaune bata kare mana ba a wannan kasa. Dan na tabbata wata rana wata shafaffiya-da-man in taci ta koshi, cewa za tayi a kamo mata shugaban sojoji.

Categories
Siyasa

Gwamnatin tarayy Najeriya tace zata ƙarawa Ma aikata Albashi Ministan Gwadago-Ngige

Ministan ƙwadago na Najeriya Chris Ngige ya ce nan ba da jimawa ba gwamnatin tarayya za ta bayyana ƙarin albashi ga ma’aikatan gwamnati a ƙasar domin rage raɗadin tashin farashin kayyaki da ake fuskanta a ƙasar.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da manema labarai jim kaɗan bayan ya yi wata ganawar sirri da shugaban ƙasar Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Villa.

Ya ce kwamiti kan albashi da shugaban ƙasar ya kafa na sake duba batun albashin ma’aikata a ƙasar, kuma ana sa ran zai zo da buƙatar ƙarin albashin a shekara mai kamawa.

Da aka tambaye shi sun tattauna wannan batu tare da shugaba Buhari, sai ministan ya ce ”ƙwarai kuwa, wannan shi ne abin da nake faɗa cewa kwamitin albashi da shugaban ƙasar ya kafa na aiki kafaɗa-da-kafaɗa da hukumar albashin ma’aikata ta ƙasar”.

“Dan haka yayin da muka shiga sabuwar shekara gwamnatin tarayya za ta ayyana batun ƙarin albashin”, in ji ministan.

Kan batun albashin wata takwas da malaman jami’o’in ƙasar ke buƙatar gwamnati ta biya su kuwa, Ministan ya ce batun na gaban kotu.

Article share tools

Categories
Siyasa

This is morning in kano Rabiu Musa Kwankwaso visit to the Hon Ghali Umar

Rabi’u Musa and Ghali Umar

This morning in Kano, I paid a condolence visit to the former Speaker of the House of Representatives, Rt. Hon. Ghali Umar Na’abba who lost his mother, Hajiya Rabi, last week.

May Allah grant her soul eternal rest and make Jannatul Firdaus her final abode. – RMK

Categories
Siyasa

Who are the biggest influences in your life?

Categories
Siyasa

Yan bindiga sun tashi ofishin jam’iyyar PDP a Gombe.

Jamiyyar PDP mai hammaya a jihar Gombe ta ce wasu da ake zargim yan bangar siyasa sun cina wuta a ofishin yakin neman zaben dan takararta na gwamnan jihar Mohamed Barde da tsakar daren Litinin.

PDP ta kuma ce wannan ba shi ne karon farko da ake kai wa ofishinta hari ba.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta ce ta soma gudanar da bincike a kan lamarin.

Babu dai cikakkun bayanai kan harin, amma dai PDP ta zargi APC da wannan hari.

A sanarwar da ta fitar, Mohammed Barde ya ce sun tafka asara sosai a harin.

Sai dai babban jami’in yada labaran gwamna mai ci Inuwa Yahaya, ya ce PDP kawai na neman abin tallata kansu ne.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Gombe, ASP Mahid Mu’azu Abubakar, ya ce sun kaddamar da bincike kan lamarin.

Categories
Siyasa

Yan bindiga sun yi dirar Mikiya a gidan shugaban kwamitin yaƙin Zaɓen PDP

‘Yan bindiga sun kai hari gidan shugaban kwamitin yaƙin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Lee Maeba a jihar Ribas.

Sun lalata motoci sama da biyar a gidan, a harin da suka kai jiya Alhamis da safe.

Shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar ta PDP a Ribas, ya tabbatar wa gidan talabijin na Channels faruwar lamarin, inda ya ce wani mutumi ne ya kira sa tare da fada masa cewa ya yi taka tsan-tsan kan yunkurin kawo harin.

Ya ce an kawo harin ne jim kadan bayan fitar sa zuwa gidan surukansa, inda suka yi ta harbe-harbe a kofar gidan tare da daure maigadin gidan.

An ruwaito raunata mutum akalla uku yayin harin.

Babu wata sanarwa daga wajen ‘yan sanda kan harin lokacin hada rahoton, sai dai, gwamnatin Ribas ta umurci jami’an tsaro da su gudanar da bincike kan lamarin.

Article share tools

Categories
Siyasa

Ko dan magoya bayan ka rege kuɗin shiga jami’ar ka – Sen.Kwankwaso

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya roki abokin karawarsa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, da ya rage kudin makaranta a jami’arsa, wanda dubban ‘yan Najeriya magoya bayansa zasu samu damar samun ilimi.

Kwankwaso ya bayyana haka ne ranar Lahadi yayin da yake amsa tambayoyi kan yadda za a inganta bangaren ilimi a wani taron da gidan Talabijin na Arise TV ta gayyacesu tare da hadin guiwar cibiyar damokaradiyya da cigaba da jaridar Vanguard.

“Dole ne inyi godiya ga Waziri, yana da jami’a wacce take da kyau sosai. Abu daya da ya dace yayi kokarin yi shi ne ya yi kasa da kudin makarantar ta yadda magoya bayansa da ‘yan Najeriya masu yawa zasu iya shiga.”

Kwankwaso ya kara da cewa, zai karfafa bangarori masu zaman kansu da su zuba hannayen jari a fannin ilimi tun daga firamare har zuwa jami’a yayin da yace komai dangane da ASUU dole ne ya zamo na gaskiya.

A yayin amsa tambayar, Atiku ya tsaya kan cewa ilimi yafi komai amfani cikin abubuwan da ya dace yara su samu ta yadda za a habaka cigaban kasa yayin da ya jaddada cewa a zuba kudi masu yawa a bangaren ilimi.

“Abu mafi muhimmanci shi ne a ilimantar da yaranmu. Kuma ba ilimi kawai ba, yadda ya dace. Daga nan ne zasu iya bada gudumawa a fannin cigaban bangaren wanda shi ne tushen tattalin arziki.”

Atiku ya kara da bada misali kan yadda aka kirkiro UBEC yayin da yake mataimakin shugaban kasa wanda ya zama wajibi ga kowanne yaro ‘dan Najeriya da ya samu ilimin firamare zuwa karamar sakandare kyauta.

Jami’ar Amurka (ABTI) dake Najeriya a garin Yola dake jihar Adamawa, mallakin Atiku Abubakar ce, jaridar Vanguard ta rahoto

Design a site like this with WordPress.com
Get started