Categories
Labaran Duniya Nishadi Rahoto Siyasa Wasanni

Mutane 15 doka tasa halewa ayi musu jiniya a Najeriya -Abba Hikima

Duk Nigeria mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya. A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa. Kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata sahalewa ba zaman gidan yari ne na wata 6.

Barin mutanen da basu cancanci a musu jiniya ba yin amfani da ita yana kara kumbura musu kai. Yana sa su girman kai da raina mutane. Kuma ya jawo raina doka.

Saboda haka, ya kamata yan sanda su kama wannan mata su gurfanar da ita a gaban kotu a bisa wannan laifi da sauran laifuffukan da suka fito fili.

Kuma indai shugabanni; zababbu da nadaddu basu takawa matan su da iyalan su birki akan shiga harkokin mulki ko bawa jami’an Nigeria umarni ba, to zaune bata kare mana ba a wannan kasa. Dan na tabbata wata rana wata shafaffiya-da-man in taci ta koshi, cewa za tayi a kamo mata shugaban sojoji.

Categories
Wasanni

Filin wasa mafi girma dake ƙasar Qatar wanda za’a fafata wasan Ƙarshe a Yau

Wannan ƙaya tattun hotunan filin wasa da za a Ƙarƙare kasar cin kofin duniya a Dake ƙasar QATAR

Wannan ne filin wasa na Lusail Inda za’ayi fafa tawar ƙarshe a gasar cikin Duniya ta shekara 2022  tsakanin ƙasar Ajantina da ƙasar Faransa za a buga wannan wasan a Yau Lahadi da misalin karfe’ 4:00mp Agogon Najeriya Nijar Kamaru da ƙasar Chadi

Lusail filin wasane na musamman wanda a kafi Sani da  Lusail Iconics Stadium filin wasa mafi Girma a ƙasar Qatar wanda yake cin Mutane sama da dubu 80,000 kuma na da nisan kilomita Ɗaya 1 wanda ka gina da Kwanon gwal  tare da talafin durakun  Ƙarfe 24.

Categories
Wasanni

Da yiwuwar ɗan wasa Neymar ka iya buga kasar cin kofin Duniya

Watakila Neymar ya buga wasan da Brazil za ta fafata da Koriya ta Kudu ranar Litinin a karawar zagaye na biyu a Gasar Cin Kofin Duniya a Qatar.

Mai shekara 30 bai yi wa Brazil wasan da ta ci Switzerland ba da wanda Kamaru ta yi nasara a fafatawar cikin rukuni na bakwai.

Dan kwallon mai taka leda a Paris St Germain ya ji rauni a wasan farko a cikin rukuni da Brazil ta ci Serbia 2-0.

Brazil wadda ake sa ran za ta iya daukar kofin Qatar ta kai zaga na biyu tun kan ta fuskanci Kamaru a wasan karshe a rukuni na bakwai.

Koriya ta Kudu kuwa ta yi ta biyu ne a rukuni na takwas da maki hudu.

Wannan shi ne wasa na takwas da za a kece raini tsakanin tawagogin biyu, amma na farko a babbar Gasar tamaula ta Duniya.

Brazil ta yi nasara a wasa shida aka doke ta karawa daya – wasan karshe da suka fuskanci juna shi ne a watan Yuni, inda Brazil ta ci 5-1.

Duk wadda ta yi nasara a wasan Litinin za ta buga daf da na kusa da na karshe tsakanin Japan da Croatia.

Croatia ita ta yi ta biyu a Gasar Kofin Duniya da aka yi a Rasha a 2018, wanda Faransa ta lashe.

Categories
Wasanni

Pogba yace ba zai Bugawa Faransa Gasar Kofin duniya ba

Dan wasan Juventus, Paul Pogba ba zai buga wa Faransa gasar cin kofin duniya a Qatar, bayan da bai murmure daga jinyar gwiwar kafa ba.

Pogba mai shekara 29, bai yi wasa ko daya ba a Serie A ta kakar nan, tun bayan da ya sake komawa Juventus daga Manchester United a kakar nan.

Ya ji raunin a gwiwar kafarsa a cikin watan Yuli, wanda bai amince a yi masa aiki ba a lokacin don gudan kada ya kasa zuwa gasar kofin duniya.

Qatar za ta karbi bakuncin babbar gasar tamaula ta duniya daga ranar 20 ga watan Nuwamba zuwa 18 ga watan Disambar 2022.

Faransa mai rike da kofin za ta fara wasa da Australia ranar 22 ga watan Nuwamba.

Pogba wanda rabon da ya yi wa Faransa tamaula tun bayan doke Afirka ta Kudu 5-0 a wasan sada zumunta cikin watan Maris, ya koma atisaye a farkon watan jiya.

Amma sai ya kasa motsa jiki yadda ya kamata, hakan ya sa ya yanke shawarar da likitoci su yi masa tiyatar.

Tawagar Faransa ta lashe kofin duniya a Rasha a 2018 tare da Pogba a lokacin.

Categories
Wasanni

Man City ta lallasa Man United da Kwallaye A. Gasar premier

Manchester City ta doke Manchester United da ci 6-3 a wasan makon na takwas a gasar Premier League da suka kara ranar Lahadi a Etihad.

Tun kan hutu City ta ci kwallo 4-0 ta hannun Phil Foden da Erling Haaland kowanne ya ci bibiyu.

Bayan da suka huta suka koma karawar zagaye na biyu Foden da Haaland kowanne ya kara zura kwallo a raga.

Sai dai United ta zare uku ta hannun Dos Santos, sannan Anthony Martial ya zura biyu a raga daya daga ciki a bugun fenariti.

Da wannan sakamakon City tana mataki na biyu a kan teburin Premier da maki 20, United kuwa tana nan da makinta 12 tana ta shida a teburin wasannin bana.

Manchester City ta yi nasara karo uku a jere a kan United tun bayan doke ta hudu da ta yi tsakanin Afirilun 2013 zuwa Nuwambar 2014.

United ta yi rashin nasara karo na 18 a Premier League a hannun City, – Liverpool da Chelsea sun yi nasara a kan United irin haka a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Wasan da suka fafata a bara:

2021/2022

Premier League Lahadi 6 ga watan Maris 2022           

  • Man City         4 – 1     Man Utd         

Premier League 6 ga watan Nuwamba 2021         

  • Man Utd          0 – 2     Man City
Design a site like this with WordPress.com
Get started