Dan wasan Juventus, Paul Pogba ba zai buga wa Faransa gasar cin kofin duniya a Qatar, bayan da bai murmure daga jinyar gwiwar kafa ba.
Pogba mai shekara 29, bai yi wasa ko daya ba a Serie A ta kakar nan, tun bayan da ya sake komawa Juventus daga Manchester United a kakar nan.
Ya ji raunin a gwiwar kafarsa a cikin watan Yuli, wanda bai amince a yi masa aiki ba a lokacin don gudan kada ya kasa zuwa gasar kofin duniya.
Qatar za ta karbi bakuncin babbar gasar tamaula ta duniya daga ranar 20 ga watan Nuwamba zuwa 18 ga watan Disambar 2022.
Faransa mai rike da kofin za ta fara wasa da Australia ranar 22 ga watan Nuwamba.
Pogba wanda rabon da ya yi wa Faransa tamaula tun bayan doke Afirka ta Kudu 5-0 a wasan sada zumunta cikin watan Maris, ya koma atisaye a farkon watan jiya.
Amma sai ya kasa motsa jiki yadda ya kamata, hakan ya sa ya yanke shawarar da likitoci su yi masa tiyatar.
Tawagar Faransa ta lashe kofin duniya a Rasha a 2018 tare da Pogba a lokacin.
Bayanan hoto,Muhammadu Sanusi ya ce “dole ne sai an shiga mawuyacin hali” kafin a gyara Najeriya
Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya Muhammadu Sanusi II ya gargaɗi ‘yan ƙasar cewa gyaran Najeriya ba abu ne mai sauƙi ba, yana mai cewa duk ɗan takarar da ya faɗi akasin haka “ƙarya yake yi”.
Kazalika Sanusi, wanda sarkin Kano ne mai murabus, ya shawarci masu jefa ƙuri’a da kar su zaɓi duk ɗan siyasar da ya ce gyaran Najeriya abu ne mai sauƙi.
“Matakan da za a ɗauka na gyara wannan [Najeriya] ba za su yi daɗi ba,” in ji shi yayin da yake magana a taron zuba jari da gwamnatin Jihar Kaduna ta shirya ranar Asabar.
Taron ya samu halartar manyan baƙi kamar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC mai mulki, da Gwamnan Jigawa Abubakar Badaru, da Gwamnan Kebbi Atiku Bagudu da sauransu.
Haka nan, Ƙaramar Ministar Kasuwanci Mariam Yalwaji Katagum ce ta wakilci Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a wurin taron da ake kira KadInvest, wanda ake gudanarwa shekara-shekara karo na bakwai – 7.0.
‘Ko dai ƙarya yake yi muku ko kuma bai san aikin ba’
Bayanan hoto,Muhammadu Sanusi ne mataimakin shugaban hukumar zuba jari ta Kaduna
Sanusi Lamido Sanusi – wanda a yanzu ake kira Muhammadu Sanusi – shi ne mataimakin shugaban hukumar zuba jari ta Kaduna mai suna Kaduna Investment Promotion Agency.
Da yake gabatar da jawabinsa, tsohon gwamnan na CBN ya ce ganin yadda ake samun raguwa a kuɗaɗen haraji da kuma ɗumbin bashin da ake bin Najeriya, wajibi ne a ɗauki “matakai masu tsauri”.
“Matakan da za a ɗauka dole ne su zama masu tsauri. Saboda haka bari na shawarci ‘yan siyasarmu, dole ne ku faɗa wa ‘yan Najeriya gaskiya game da mawuyacin halin da za a shiga.
“Duk wanda ya faɗa muku cewa cikin sauƙi za a yi gyara kar ku zaɓe shi, saboda ko dai ƙarya yake yi muku ko kuma bai san irin aikin da ke gabansa ba.”
Sarkin na Kano mai murabus yana ganin cewa lallai sai an gyara tsarin biyan kuɗin lantarki da farashin man fetur, yana mai cewa “ana zuzuta yawan man da ‘yan Najeriya ke sha a kullum”.
A cewarsa: “Wajibi ne sai an ɗauki matakan da suka dace. Amma kafin a yi hakan, dole sai an gyara adadi na ƙarya da ake bayyanawa, sai an yaƙi cin hanci.”
Abin da sabon shugaban ƙasa ya kamata ya fara yi
Da ma an san Sanusi da ra’ayin goyon bayan cire tallafin man fetur, wanda bai gushe ba sai da ya yi kira ga duk wanda ya yi nasarar zama shugaban ƙasa a 2023 da ya yi bincike a ɓangaren tallafin.
Ya ce: “Ina fatan duk wanda ya zama shugaban ƙasa a 2023, abin da zai fara yi shi ne ya nemi kamfanin mai na NNPC ya yi bayani kan duk dalar da ya karɓa a matsayin kuɗin tallafin mai.
“Dole ne su ba da bayanan jiragen ruwan da suka shigo wanda kuma za a iya tabbatarwa daga kamfanonin inshora ko da gaske ne jirgin ya sauka a Najeriya a wannan ranar.
Kar ku zaɓi duk ɗan takarar da ya ce gyaran Najeriya abu ne mai sauƙi – Sanusi
“Saboda doka ta ce dole ne sai an nuna hujja kafin a karɓi kuɗin tallafi kuma dole ne sai an ba da hujja cewa an kawo man a kan farashin da mutum ya ce ya kawo shi. Haka doka ta ce.”
Tuni gwamnatin Buhari ta ce ta shirya daina biyan tallafin daga tsakiyar shekarar 2023, daidai lokacin da zai bar mulki bayan ya shafe wa’adi biyu na shekara takwas jimilla.
Rahotanni sun nuna cewa gwamnati na kashe fiye da naira tiriliyan ɗaya duk wata wajen biyan tallafin fetur, abin da masana tattalin arziki irin su Muhammadu Sanusi ke cewa gara a karkatar da su kan ayyukan raya ƙasa.
Bayanan hoto,Ministan Ƙwadago Chris Ngige ke nan yayin da yake miƙa wa shugabannin ƙungiyoyin NAMDA da CONUA
A ranar Talata ne gwamnatin Najeriya ta yi wa ƙungiyar malaman jami’a ta ASUU kishiya da sabuwa mai suna Congress of Nigerian University Academics (CONUA) rijista, abin da ya jawo martani iri-iri daga ƙwararru da ma ‘yan ƙasa baki ɗaya.
Kazalika, Ministan Ƙwadago Chris Ngige ya bai wa National Association of Medical and Dental Academics (NAMDA) shaidar rijista, duka da zummar rage wa ASUU ƙarfin iko, kamar yadda masu sharhi ke cewa.
Mista Ngige ya ce ƙungiyoyin za su ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da ASUU a jami’o’in ƙasar.
Gwamnatin ta ɗauki wannan mataki ne yayin da kotu ta ba da umarnin a sasanta rikicin a wajen kotun gwamnati ta kai ƙarar ASUU gaban kotun ɗa’ar ma’aikata.
Shi ma Shugaba Muhammadu Buhari da kansa ya zargi malaman jami’a da cin hanci da yin lalata da ɗalibai don ba su makin jarrabawa.
ASUU ta fara yajin aiki tun daga watan Fabarirun shekarar nan ta 2022 tana neman ƙarin albashi da kuɗaɗen farfaɗo da jami’o’i da kuma alawus-alawus.
Shahararren lauya mai gwagwarmayar kare haƙƙi, Femi Falana, ya ce rijistar da aka yi wa ƙungiyoyin ta saɓa wa doka.
A cewarsa, “dokar ƙwadago ta Najeriya ba ta ba da damar yi wa ƙungiya sama da ɗaya rijista a sashe ɗaya ba”.
Tun bayan da aka samu Ambaliyar Ruwan Babban dam a jahar Kano ya tafi da manyan manyan fayif ɗin dake ɗauko ruwa Daga dam zuwa Injinan dake tace ruwa.
Har zuwa yanzu shiru ka keji kamar an aiki bawa Garin su ya kamata Gwamnatin jahar Kano tudu ba na tsana ki Dan magance wannan matsala taruwan sha da jama’a ke fama da ita .
Tsohon dakataccen shugaban hukumar karbar ƙorafe-ƙorafe da yaƙi da rashawa ta jihar Kano, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana cewa, sun tattauna da shugaban jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano, Umar Haruna Doguwa, da kuma shugaban jam’iyyar na karamar hukumar Rimin Gado, domin ganin yadda za’a ciyar da Kano gaba.
Cikin wani saƙo da ya wallafa yau a shafinsa na sada zumunta, an hangi fuskokinsu cike da annuri da walwala.
Muhuyi dai ya fice daga jam’iyyar APC bayan wata tashin-tashina da ta faru tsakaninsa da gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, inda ya kowa jam’iyyar PDP har ya siyo tikitin neman takarar gwamnan Kano.
Manchester City ta doke Manchester United da ci 6-3 a wasan makon na takwas a gasar Premier League da suka kara ranar Lahadi a Etihad.
Tun kan hutu City ta ci kwallo 4-0 ta hannun Phil Foden da Erling Haaland kowanne ya ci bibiyu.
Bayan da suka huta suka koma karawar zagaye na biyu Foden da Haaland kowanne ya kara zura kwallo a raga.
Sai dai United ta zare uku ta hannun Dos Santos, sannan Anthony Martial ya zura biyu a raga daya daga ciki a bugun fenariti.
Da wannan sakamakon City tana mataki na biyu a kan teburin Premier da maki 20, United kuwa tana nan da makinta 12 tana ta shida a teburin wasannin bana.
Manchester City ta yi nasara karo uku a jere a kan United tun bayan doke ta hudu da ta yi tsakanin Afirilun 2013 zuwa Nuwambar 2014.
United ta yi rashin nasara karo na 18 a Premier League a hannun City, – Liverpool da Chelsea sun yi nasara a kan United irin haka a babbar gasar tamaula ta Ingila.
Hukumar zaɓen Najeriya INEC ta bayyana cewa dole jam’iyyun ƙasar da aka yi wa rajista su bayyana inda suka samu kuɗin kamfe ɗinsu da kuma bin ƙa’idojin da aka gindaya na kashe kuɗi a lokacin yaƙin neman zaɓe.
Shugaban na INEC Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a yayin wata hira da gidan talabijin na Trust TV a Najeriya inda ya ce akwai kuma adadin da aka ƙayyade na irin gudunmawar kuɗi da mutum zai iya bai wa jam’iyya a yaƙin neman zaɓe.
Haka kuma ya ƙara jaddada cewa jam’iyyu ba za su iya karɓar tallafin kuɗi ba daga ƙasashen waje.
A cewarsa, idan ma an samu irin wannan tallafin, ya zama dole a tura wa hukumar zabe waɗannan kuɗaɗe.
Ana gudanar da zaɓe a ƙasar Bulgaria wanda wannan shi ne karo na huɗu da ake zaɓen ƴan majalisa a cikin watanni 18 a ƙasar.
Manyan abubuwan da za a mayar da hankali a kansu sun haɗa da hauhawar farashi da yaƙin Ukraine da wahalar makamashi da kuma yaƙi da cin hanci da rashawa.
Gwamnatocin haɗaka na baya sun sha fama da matsalolin da suka haɗa da cin hanci da rashawa.
Haka kuma akwai rabuwar kai tsakanin masu goyon bayan jam’iyyun da ke goyon bayan ƙasashen yamma da kuma masu goyon bayan Rasha.
Za a gudanar da wannan zaɓe ne bayan rushewar gwamnatin Kiril Petkov wadda ta shafe watanni shida kacal tana kan mulki.
Ƙoƙarin da ya yi na gyara albashi ya bi ruwa sakamakon hauhawar farashi.
Koriya ta Arewa ta sake harba makamai ma su linzami guda biyu zuwa Tekun Gabashin Chaina, kwanaki biyu bayan wani gwajin makami mai linzami da ta yi.
Wannan sabon gwajin makaman dai, na zuwa ne gabanin ziyarar da mataimakiyar shugabar Amirka Kamala Harris za ta kai makwabaciyar Koriya ta Arewan kana abokiyar tagwaitakarta da kuma takun sakarta Koriya ta Kudu. Rundunar sojojin Koriya ta Kudun ta bayyana cewa, ta gano makamai masu linzami da ba sa cin dogon zango guda biyu da aka harba daga fadar Pyongyang. Rahotanni sun nunar da cewa an harba makami na biyu, mintuna 10 bayan harba na farko.