Categories
Siyasa

Mun samu tattaunawa da Shugaban jam’iyar NNPP Na jahar Kano-Magaji Rimin Godo

Tsohon dakataccen shugaban hukumar karbar ƙorafe-ƙorafe da yaƙi da rashawa ta jihar Kano, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana cewa, sun tattauna da shugaban jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano, Umar Haruna Doguwa, da kuma shugaban jam’iyyar na karamar hukumar Rimin Gado, domin ganin yadda za’a ciyar da Kano gaba.

Cikin wani saƙo da ya wallafa yau a shafinsa na sada zumunta, an hangi fuskokinsu cike da annuri da walwala.

Muhuyi dai ya fice daga jam’iyyar APC bayan wata tashin-tashina da ta faru tsakaninsa da gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, inda ya kowa jam’iyyar PDP har ya siyo tikitin neman takarar gwamnan Kano.

Sauran bayanai nanan tafe…

Design a site like this with WordPress.com
Get started